Gwamnatin Jigawa da Katsina Sun Saka Dokar Hana Fita 

 

Jihar Jigawa – Gwamnatin jihar Jigawa ya sanya dokar zaman gida ta tsawon sa’o’i 24 yayin da zanga-zangar lumana ya riƙide ta zama tashin hankali ranar Alhamis.

Gwamnan Jigawa, Malam Umar Namadi Ɗanmode ne ya sanar da ƙaƙaba dokar a wani jawabi na kai tsaye da ya yi ranar Alhamis da daddare.

A ranar farko ta zanga zangar yunwa wadda masu shiryawa suka ce ta lumana ce, an yi kashe-kashe, kone-kone da satar dukiya a jihohi da dama ciki hada Jigawa.

Domin daƙile yaɗuwar ɓarnar da aka yi  Gwamna Umar ya sanya dokar kulle a faɗin kananan hukumomin jihar, kamar yadda Leadership ta kawo.

Gwamnan ya bayyana halin da ake ciki, a jihar a matsayin abin takaici matuka kuma ba zai zama mafita ga bukatun mutane ba.

Ita ma gwamnatin jihar Katsina ta sanya dokar hana fita na sa’o’i 24 a ƙaramar hukumar Dutsima, yayinda ta hana zirga-zirgar mutane daga ƙarfe bakwai na yamma zuwa ƙarfe bakwai na safe a sauran ƙananan hukumomin 33 da ke jihar.

Karin bayani na nan tafe…

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here