A Gaggauta Karbe Makamai da Kwayoyi a Hannun Matasan Fulani Domin Magance Garkuwa da Mutane- Janar Dambazau

Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau (mai ritaya) ya yi kira ga cewa a yi gagawan raba matasan Fulani da kwayoyi da makamai.

Dambazau wanda tsohon minista ne na harkokin cikin gida kuma babban hafsan sojojin kasa ya yi wannan kiran ne a wani taro a Abuja.

Tsohon ministan ya jaddada bukatar da ke akwai na daukan matakai domin magance garkuwa da mutane tsakanin matasa fulani a Najeriya.

FCT, Abuja – Tsohon ministan harkokin cikin gida, Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau (mai ritaya) ya bukaci a gaggauta karbe makamai da kwayoyi a hannun matasan Fulani a matsayin wani mataki na dakile garkuwa da mutane a kasar.

Dambazau ya yi wannan kiran ne a kasidar da ya gabatar mai taken “Matsalar Makiyaya Fulani” da ya gabatar a taron tsaro na makiyaya fulani a Abuja.

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa an yi taron ne da nufin gano hanyoyi warware kallubalen da makiyaya fulani ke fuskanta a zamanin nan da nufin samar da tsaro a kasar.

An shirya taron ne da hadin gwiwa da kungiyar Miyetti Allah da Northern Consensus Movement, NCM.

A cewarsa, daya daga cikin matakan da za a dauka shine dakile samun makamai da kwace dukkan makaman da a yanzu ke hannun matasan fulani makiyaya.

Kalamansa:

“Ya kamata mu tsaftace kasar, ina nufin da taimakon NDLEA, ya kamata a yi yaki da shan miyagun kwayoyi a tsakanin matasan fulani.

“Ya kamata mu tabbatar da adalci da cigaban al’umma da ilimi da lafiyan makiyaya fulani tare da basu damar cigaba a cikin al’umma.

“Don cimma hakan, ya kamata a basu ingantaccen ilimi, lafiya da kuma koyar da su sana’o’i.”

Ya ce wata matsala kuma shine wasu makiyayan da ke zama a daji suna satar mutane don karbar kudin fansa.

Ya kara da cewa:

“A baya ana iya gane makiyayi da sandarsa da ya ke kiwon shanu, a yau da AK-47 da wasu makaman ake ganinsu kuma suna amfani da shi wurin kai wa mutanen kauyuka hari ko garkuwa da fasinjoji a manyan hanyoyi.

“An san makiyayi fulani da saukin kai, tausayi, gaskiya, da sadaukarwa amma a yau ana masa kallon dan fashin daji, makashi, mai fyade, barawon shanu da mai garkuwa.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here