Jam’iyyar Islama ta Karama: Kotun Sojoji a Tunisia ta Daure ‘Yan Majalisar Dokoki 2

 

Wata kotun sojoji a Tunisia ta daure wasu ‘yan majalisar dokoki biyu daga jam’iyyar Islama ta Karama.

An zargi Nidal Saudi da cin mutuncin ma’aikatan tsaro a filin jirgin sama, kuma an hukunta Saif Eddine Makhlouf saboda yi wa alkali barazana da kuma yin wasu kalamai a kotu.

Mista Makhlouf yana yawan sukar shugaban Tunisia, Kais Saied.

Kwanan nan shugaban ya dakatar da majalisar kuma ya kwace kusan dukkan iko a hannunsa, lamarin da ya haifar da karuwar damuwa game da tabarbarewar hakkin dan adam a kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here