Kotu ta Gurfanar da Wani Dan Majalisa

Kotun majistare da ke yankin Wuse, Zone 6, ta gurfanar da mamba majalisar wakilai daga mazabar Billiri/Balanga a jihar Gombe, Mista Victor Mela.

– Rundunar ‘yan sanda a birnin tarayya ta rubuta korafin zargin Mista Mela da rantsuwa a kan karya yayin da ya cike fom din INEC

– Lauyan da ke kare dan majalisar ya bukaci kotu ta yi sassauci a hukuncin da za ta zartar a kan Mista Mela

Wata kotun majistare da ke zamanta a Wuse, Zone 6, ta gurfanar da mamba a majalisar wakilai, Mista Victor Mela, bisa zarginsa da bayar da bayanan karya ga hukumar zabe ta kasa (INEC) tare da yin rantsuwa a kan cewa gaskiya ne.

Kotun ta ce dan majalisa Mela, mai wakilatar mazabar Billiri/Balanga a majalisar tarayya, ya bawa INEC bayanan karya domin samun damar tsayawa takara a zaben shekarar 2019.

Hukumar ‘yan sandan birnin tarayya (FCT), Abuja, ce ta gurfanar da Mista Mela bayan zarginsa da rattaba hannu, a matsayin rantsuwa, a kan bayanana karya da ya bayar yayin cike fom din hukumar INEC mai lamba CF001 gabanin zaben 2019

Alkalin kotun da ya saurari karar ya saka ranar yanke hukunci a kan karar bayan lauyan da ke kare Mista Mela ya nemi kotu ta yi sassauci a hukuncin da za ta zartar a kan wanda ya ke karewa.

Hukumar INEC ta bayyana Mista Mela a matsayin wanda ya samu nasarar lashe zaben kujerar zaben dan majalisar wakilai na mazabar Billiri/Balanga a zaben da aka gudanar a cikin watan Fabarairu na shekarar 2019.

Duk da Ali Isa, dan takarar jam’iyyar PDP, ya kalubalanci nasarar da Mista Mela ya samu a zaben, kotun turabunal da ta daukaka kara da ke Jos sun jaddada nasarar da dan takarar na APC ya samu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here