Ministar Raya Al’adu: An Buƙaci Kotu ta Soke Naɗin da aka yi wa Hannatu Musawa

 

Wata ƙungiyar farar-hula da ake kira ‘Incorporated Trustees of Concerned Nigerians’ ta kai sabuwar ministar raya al’adu, Hannatu Musa Musawa Kotu inda ta buƙaci a soke naɗin da aka yi mata.

Ƙungiyar ta kare manufofinta kan bukatar hakan, saboda korafe-korafen da suka biyo bayan gane cewa ministar ba ta kammala aikin yi wa ƙasa hidima ba wato NYSC.

Masu shigar da karar karkashin jagorancin Deji Adeyanju sun buƙaci kotu ta duba kundin tsarin mulkin ƙasa ta fayyace musu idan mutum na iya haɗa aikin hidimar ƙasa ta NYSC da kuma muƙamin minista a lokaci guda.

Sannan sun buƙaci a ci tarar ministar naira miliyan 100 da kuma naira miliyan ɗaya kuɗin ɓata lokaci a kai ta kotu.

Takardun da suka miƙawa kotu mai shafi 13 sun kuma bayyana cewa, Hannatu Musawa ta amsa cewa yanzu take NYSC ɗinta, kuma an tura ta Abuja domin hidimtawa ƙasa.

Korafin nasu na jadadda cewa babu dokar NYSC da ta amince mai hidimatawa ƙasa ya karɓi wani aiki na gwamnati ko muƙamin siyasa.

Ƙungiyar ta ce ya zama wajibi a yi adalci wajen wannan shari’a.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com