Jam’iyyar Macron ta Rasa Kusan Kujeru 100 a Majalisar Dokokin Faransa

 

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya samu gagarumin koma-baya a siyasa, bayan da gwamnatinsa ta hadaka ta rasa rinjaye a majalisar dokokin kasar.

Jam’iyyarsa ta hadakar ta rasa kusan kujeru 100 a majalisar, yayin da jam’iyyar Marine Le Pen ta masu tsatstsauran ra’ayin rikau da kuma jam’iyyar masu tsattsauran ra’ayin kawo sauyi ta Jean-Luc Mélenchon suka samu kujeru da dama a majalisar.

Mr Melenchon ya kasance shi ne babban abokin hamayyar Mr Macron a zaben shugaban kasar da aka yi a watan Afrilu, inda a yanzu kuma ya zamo jagoran ‘yan adawa.

Kasa da wata biyu kenan da Mr macron ya sake lashe zaben shugaban kasa a karo na biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here