Kwale-Kwale ya Nutse da Mutane 6 Ciki Har da Mai Juna Biyu a Bayelsa

Rahotanni daga yankin karamar hukumar Ijaw ta Kudu a jihar Bayelsa da ke Kudancin Najeriya na cewa mutum shida da suka hada da wata mace mai ciki sun nutse a ruwa, bayan da kwale-kwalensu ya kife.

Hatsarin ya faru ne ranar Asabar da rana.

Jaridun cikin gida sun ruwaito cewa yanzu haka masu aikin ceto na kan neman matafiyan, da suka hada da wata mai hidimar kasa da kuma dattijuwa mai shekara 70.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sanda a jihar Bayelsa, SP Asinim Butswat, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kara da cewa suna jiran karin bayani kan bayanan mutanen da lamarin ya rutsa da su.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here