Kotun ƙoli ta Sanya Rana Kan Shari’ar Jam’iyyar ADC

 

Kotun ƙolin Najeriya ta sanya ranar 22 ga watan Afrilun 2026 a matsayin ranar da za ta saurari ƙarar da David Mark da wasu shugabannin jam’iyyar ADC suka ɗaukaka a gabanta game da rikicin shugabanci da jam’iyyar ke fama da shi.

Kotun, ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Mohammed Garba ta ajiye ranar ne bayan amincewa da gaggauta sauraron shari’ar.

Daga nan ne sai kotun – wadda ta zauna a yau Talata – ta bai wa lauyan David Mark, Jibril Okutepa umarnin ya tattara bayanansa da miƙa su ga kotu ya zuwa gobe Laraba.

Sannan kotun ta buƙaci lauyan waɗanda ake ƙara su miƙa nasu martanin gare ta a cikin kwana uku.

David Mark ya daukaka ƙara ne game da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na ranar 12 ga watan Maris, wanda ya yi watsi da ƙarar da ya ɗaukaka game da hukuncin babban kotun tarayya na ranar 4 ga watan Satumba ƙarƙashin mai shari’a Emeka Nwite.

Babbar kotun tarayyar ta ƙi amincewa da buƙatar David Mark ta soke wasu daga cikin umarnin da kotu ta bayar bayan ƙorafin da wani ɗan jam’iyyar Nafiu Bala Gombe ya gabatar.

Ana sa ran hukuncin kotun ƙolin zai kawo ƙarshen dogon lokacin da aka kwashe ana rikici game da shugabancin jam’iyyar ta ADC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here