Rashin Tsaro: Matasa a Jahar Sokoto Sun Fito Zanga-Zanga
Matasa sun fito zanga-zanga a kan titunan garin Goronyo da ke jahar Sokoto.
Sun yi zanga-zangar ne domin neman gwamnati ta kawo musu dauki kan batun rashin tsaro.
Yawan hare-haren ‘yan bindiga yana tilastawa mazauna garin yin hijira zuwa wasu garuruwan.
Sokoto – Wasu matasa a garin Goronyo da ke karamar hukumar Goronyo a jahar Sokoto sun fito kwansu da kwarkwata a tituna suna zanga-zangar halin rashin tsaro da yankinsu ke ciki.
SaharaReporters ta rawaito cewa suna can suna zanga-zangar a lokacin hada wannan rahoton.
Wani majiya ya ce matasan sun fito zanga-zangar ne saboda kallubalen tsaro a yankin, wadda ya tilastawa mutane da dama tserewa daga garin.
Ya ce:
 “Ana yin zanga-zanga a garin Goronyo da ke jahar Sokoto. Matasa sun cika tituna suna nuna damuwarsu kan rashin tsaro da ya tilastawa mutane yin hijira barin garin.Suna can suna zanga-zangar a yanzu.”
 Hotunan da SaharaReporters ta samu sun nuna an kafa shinge a kan tituna, matasan kuma na kona tayoyi domin nuna rashin jin dadinsu game da kashe-kashe da garkuwa da mutane a yankin.
 Sokoto na daya daga cikin jahohin Arewa da ke fama da matsalar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.
 A baya-bayan nan gwamnatin jahar ta bada umurnin a toshe layukan sadarwa a wasu yankunan jahar don dakile hare-haren ‘yan bindigan.
 Toshe layukan sadarwar ya shafi kananan hukumomi kamar Dange Shuni, Tambuwal, Sabon Birni, Raba, Tureta, Goronyo, Tangaza da sauransu.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here