Shugaban NITDA ya Halarci Taro Kan Tattalin Arziki da Ministan Sadarwa Bisa Jagorancin Shugaba Buhari

Mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), a ya yin halartar taron tattalin arziƙi na ƙasar Nageriya da ƙasar Spain tare da mai girma ministan sadarwa da tattalin arziƙin fasahar zamani, Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS FIIM) a bisa jagorancin mai girma shugaban ƙasar tarayyar Nageriya, Malam Muhammadu Buhari (GCFR).

Taron wanda aka yi wa take da: “Nigeria-Spain Business & Trade Forum”, ya gudana ne a birnin Madrid na ƙasar ta Spain a wannan rana inda aka tattauna kan yadda za a samar da haɗaka a tsakanin ƙasashen biyu wajen ganin masu zuba jari kan harkokin fasahar zamani da nau’in kasuwanci sun shigo Nageriya sun zuba jari domin samarwa ƙasar ƙarin cigaban arziƙi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here