Peter Obi ya Ziyarci Gwamna Wike a Port Harcourt

 

Gabannin babban zaben shugaban kasa na 2023 mai zuwa, ana ci gaba da tattaunawa a tsakanin manyan yan siyasa.

Hotunan Peter Obi yayin da ya ziyarci Gwamna Nyesom Wike sun haddasa cece-kuce a bangaren siyasar kasar.

Ana ta rade-radin cewa Wike ya fusata kan hukuncin da Atiku Abubakar na yanke na kin daukarsa a matsayin abokin takararsa gabannin zaben mai zuwa.

Rivers – Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Mista Peter Obi, ya ziyarci gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike a Port Harcourt a ranar Laraba, 22 ga watan Yuni.

Legit.ng ta tattaro cewa sun shafe tsawon awanni suna saka labule a tsakaninsu a gidan Gwamna Wike da ke Port Harcourt, babban birnin jihar Rivers.

Ana dai ta rade-radin cewa Wike na shirin ficewa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP bayan ya fadi a zaben fidda gwanin jam’iyyar sannan kuma aka ki zabarsa a matsayin abokin takarar Atiku Abubakar, wanda zai daga tutar jam’iyyar a zaben shugaban kasa na 2023.

Tuni hotunan ganawar tasu suka karade shafukan soshiyal midimiya musamman ma a kan Twitter.

Haduwar manyan yan siyasar biyu ya haddasa cece kuce kasancewar yanzu ba a ga maciji tsakanin Wike da wasu mambobin jam’iyyarsa ta Peoples Democratic Party (PDP).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here