Rashin Yafewa Pantami Ya fi Muni Kan Laifin da Ministan ya Aikata – Garba Shehu

 

Kakakin shugaban kasa Garba Shehu ya ce wadanda ba su son su yafe wa Pantami suna da matsala.

Shehu ya ce kowane mutum yana da ikon ya sauya halayensa idan ya gano ya yi kuskure a baya.

Ya yi wannan kalaman ne a matsayin martani ga wadanda suka dage sai Pantami ya yi murabus.

duk da ya nemi afuwa ya kuma ce ya sauya tunaninsa Mallam Garba Shehu ya caccaki wadanda suke sukar Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Dr Isa Pantami saboda rashin yafe masa abin da ya yi a baya, Channels Television ta ruwaito.

Ya na ganin rashin yafewa ministan kan maganganun da ya yi na goyon bayan kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi ya fi muni kan laifin da ministan ya aikata.

Babban mai taimakawa shugaban kasar a bangaren watsa labarai ya yi wannan kalaman ne a lokacin da ya bayyana a shirin Politics Today na Channels Television a ranar Juma’a.

Ya ce,

“Ina fada maka mutanen da ke cigaba da sukarsa duk da cewa mutumin ya ce ya yi wa kansa laifi, ya yi wa mutane laifi, kuma ya nemi afuwa ya sauya tunaninsa, amma ba su son su yafe masa; sune matsalar ba shi ba.”

Kungiyoyi da mutane da dama sunyi ta sukar Pantami saboda kalaman da ya furta a baya na goyon bayan kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi.

Amma fadar shugaban kasa ta fito ta ce tana tare da Pantami da dukkan yan Nigeria domin ganin anyi musu adalci da kare hakokinsu da suka danganci sadarwa na zamani Garba ya ce ba dai-dai bane a hana mutum damar ya sauya wasu halayensa idan ya gano akwai kuskure a ciki.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here