Rundunar Sojin Najeriya ta Gano Daya Daga Cikin ‘Yan Matan Chibok da Boko Haram Suka Sace

Rundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa, ta gano wata mata da ke garari a wani yankin Borno, wacce ‘yan Boko Haram suka sace.

Rahoton soji ya ce ana kyautata zaton matar na daga cikin ‘yan matan Chibok da aka sace a shekarar 2014.

Hakazalika, an gano ta ne tare da yaro, kana ana ci gaba da bincike don gano asalin tsuhen batan ta.

Borno- Dakarun runduna ta 26 Task Force Brigade, a ranar Talata, sun gano wata Mary Ngoshe, wacce a cewar rundunar sojin Najeriya, tana daya daga cikin ‘yan matan da aka yi garkuwa da su a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke Chibok a shekarar 2014.

Ngoshe, wadda aka same ta da wani yaro da ake kyautata zaton nata ne, sojojin sun tare ta ne a lokacin da suke sintiri a kewayen Ngoshe a jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a wani sako da rundunar ya wallafa a shafin Twitter a safiyar Laraba.

Sakon ya ce:

“Dakarun 26 Task Force Brigade da ke sintiri a kewayen Ngoshe a jihar Borno a ranar 14 ga watan Yuni 2022 sun gano wata mata Mary Ngoshe da danta. Ana kyautata zaton tana daya daga cikin ‘yan matan da aka sace daga GGSS Chibok a 2014.Ana ci gaba da bincikarta.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here