Rundunar Sojoji Sun Kama Hadimin Gwamna Mai Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga a Kudancin Najeriya

 

Rundunar sojoji ta bankado wanda yake da hannu dumu-dumu a daukar dawainiyar ‘yan bindiga a yankin kudancin Najeriya.

An gano wani hadimin gwamna, Tochukwu Okeke alias Owo a matsayin mai daukar nauyin ‘Unknown Gunmen’ a kudanci.

Okeke yana da kungiya wadanda suke amfani da makaman kare dangi wurin kai wa ‘yan sanda, sojoji da fararen hula farmaki.

Kudancin Najeriya – Rundunar sojin Najeriya sun samu nasarar damko hadimin gwamna ne wanda yake kulle-kullen rura wutar ta’addanci a kudu maso gabas.

An bankado wanda ake zargin yana da hannu akan kaiwa mutanen gari da jami’an tsaro farmaki a kudu maso gabacin Najeriya.

Hadimin gwamna ke daukar nauyin ‘Unkwown Gunmen’

PRNigeria ta tattaro bayanai akan yadda wani Tochukwu Okeke alias Owo, hadimin gwamna a kudu maso gabas ya daurewa ‘yan bindiga gindi kamar yadda rundunar division 82 na sojojin Najeriya a Enugu suka bankado.

Majiyar ta sojoji ta bayyana hakan ne inda ta bukaci a boye ta, tace hadimin yana da kungiya mai makaman kare dangi kuma suna kai hari ga ‘yan sanda, sojoji da fararen hula.

Kafin a kama wasu daga cikin shugabannin su a kuma lalata sansaninsu cikin ‘yan kwanakin nan, sun kaiwa ‘yan sanda da sojoji farmaki a Enugu ciki har da ofishin ‘yan sanda na Adani, wata matsayar sojoji dake kan titin Adani-Omoh, ofishin ‘yan sanda na Ezeagu, sansanin sojoji dake titin Orji River-Udi da wata dake kan titin Enugu Abakaliki.

Kungiyar ‘yan ta’addan wacce aka fi sani da “mugaye marasa imani” suna satar makamai a wurin jami’an tsaron da suke kaiwa farmaki.

Majiyar ta sanar da PRNigeria cewa an ragargaji daya daga cikin sansanayensu dake Akpawfu-Amangwunze dake karamar hukumar Nkanu ta yamma inda aka kwato makamai da dama da ababen hawa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here