Hukuncin da Ƴan sandan Somaliya Suka Dauka Kan Mata Masu Saka Niƙabi

 

Ƴan sanda a birnin Kismayo da ke kudancin Somaliya sun ce za su ɗaure ko su ci tarar matan da ke rufe fuskarsu da niƙabi saboda fargabar cewa mayaƙan Al-Shabab na iya yin shigar burtu wajen kai hare-hare.

Shugaban rundunar ƴan sanda ya ce jami’ansa sun ƙwace ɗaruruwan niƙabi cikin kwanaki huɗu da suka gabata.

An soma ƙaƙaba haramcin a 2021 sai dai galibi an yi watsi da shi.

Ranar Juma’a da daddare ne Al Shabab da ke da alaƙa da ƙungiyar al-Qaeda ta kai mummunan hari a Mogadishu babban birnin ƙasar. Mutum 37 ne suka mutu, fiye da ɗari biyu kuma suka ji rauni.

A baya-bayan nan ne sojojin Somaliya suka kashe gomman mayaƙa masu iƙirarin Jihadi a Jubaland a don haka akwai yiwuwar akai hare-haren ramuwar gayya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here