Rundunar Sojin Sudan ta Zargi Habasha da Kashe Sojojinta 7

 

Rundunar sojin Sudan ta zargi sojojin kasa na Habasha da zartar da hukuncin kisa a kan sojojinta bakwai da kuma wani farar-hula da ke tsare a hannunta.

Zargin wanda ke kunshe a wata sanarwa da kafar yada labarai ta gwamnatin Sudan ta fitar bai yi wani karin bayani ba.

Sai dai ta bayyana matakin da cewa abu ne mai hadari, kuma za a mayar da martani a kai.

Zuwa yanzu babu wani martani da hukumomin Ethiopia suka yi game da zargin na Sudan.

A cikin shekara biyu da ta gabata, rikicin da kasashen biyu suka dade suna yi a kan iyaka ya kara zafafa, inda ake samun dauki-ba-dadi, daga lokaci zuwa lokaci a tsakaninsu a yankin al-Fashaga.

Daman Sudan tana jin haushin Habasha saboda katafariyar madatsar-ruwan da kasar ke ginawa a Kogin Nilu, wanda abu ne da take ganin zai rage mata ruwan da take samu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here