Shugaba Tinubu ya Wuce Dubai Daga Indiya

 

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai ya da zango a Dubai daga taron G-20 da yake halarta a Indiya, domin ganawa da jagororin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da fadar shugaban na Najeriya ta wallafa shafinta na Twitter ta ce ganawar ci gaba ne na tataunawar jakadan ƙasar Haɗaɗdiyar Daular Larabawa ya yi da shugaba Tinubu a fadarsa da ke Abuja, domin magance wasu matsaloli na tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

Sanarwar ta kuma shugaba Tinubu zai yi ƙoƙarin magance tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

Shugaban na Najeriya ya halarci ƙungiyar taron G-20, ta ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziki na duniya bisa gayyatar firaministan Indiya, wanda ya jagoranci taron.

Shugaban zai koma Najeriya da zarar ya kammala ganawa da jagogin na UAE, kamar yadda sanarwar ta bayyana

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com