Rigakafin Corona: Gwamnatin Tarayya ta Yabawa Shugabannin CAN Bisa Goyan Bayan da ta Basu

 

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, ta fara kai allurar riga-kafin corona zuwa coci a Najeriya.

Ta kuma yabawa wasu shugabannin CAN bisa goyon bayan da suka bayar na yin allurar a coci.

Hakazalika, ga mambobin coci, gwamnati ta yaba musu wajen ba ta hadin kai don cimma burin yin riga-kafin.

Abuja – Gwamnatin tarayya a ranar Talata 14 ga watan Satumba ta sanar da shirinta na daukar allurar riga-kafin corona zuwa cibiyoyin bauta ta Kiristoci, Punch ta rawaito.

Babban Darakta na Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko, Faisal Shuaib, ya bayyana hakan ne yayin wayar da kan shugabannin Kiristoci kan kashi na biyu na riga-kafin corona a babban birnin tarayya Abuja.

Ya ce:

“Mai martaba, Shugaban CAN, fitattun shugabannin Kirista, mata da maza, ina mai farin cikin sanar da ku cewa daga wannan mataki na 2 na riga-kafin corona, mun gabatar da allurar riga-kafin ranar Lahadi.

“An yi wannan ne don tabbatar da membobin Kiristoci da watakila ba su sami damar yin allurar riga-kafi ba saboda wani dalili an ba su damar yin allurar riga-kafin a wuraren bautarsu.

“Dole ne in fadi cewa sakamako daga coci yana da kyau sosai kuma ina godiya ga dukkan shugabannin Kiristocin da suka ba kungiyar allurar riga-kafin damar zuwa majami’un su da membobin su don samun allurar corona yayin bautar ranar Lahadi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here