‘Yan Sanda Sun Sake Kama Mawallafin Sahara Reporters – Omoyela Sowore

‘Yan sandan Najeriya sun damke Omoyele Sowore a kan wata sabuwar zanga-zanga da ya fito.

An damke shi a babban birnin tarayya bayan bayyana a zanga-zangar #CrossoverWithProtest.

Tun a ranar Alhamis yayi wallafa a shafinsa na Twitter a kan gangamin a dukkan kasar nan.

‘Yan sandan Najeriya sun sake damke mawallafin Sahara reporters, Omoyele Sowore a kan jagorantar wata zanga-zanga da yayi a babban birnin tarayya na Abuja.

Sowore tare da wasu ‘yan gwagwarmaya sun shiga hannun ‘yan sandan bayan da suka fito zanga-zanga mai suna #CrossoverWithProtest, zanga-zangar da suka shirya a dukkan fadin kasar nan ana gobe sabuwar shekara.

Wasu daga cikin masu zanga-zangar da suka arce ne suka tabbatarwa da Premium Times cewa an damke Sowore inda aka jefa shi daya daga cikin motocin ‘yan sanda bakwai da aka tura wurin zanga-zangar.

Duk da majiyoyin basu san inda aka yi da Sowore ba, Sahara Reporters ta ce yana ofishin ‘yan sanda na mayanka da ke Lokogoma a Abuja tare da wasu.

Hakazalika, an yi ta kokarin samun Sowore ta lambar wayarsa amma abun ya ci tura a safiyar Juma’a.

Har a lokacin rubuta wannan rahoton, ba a san mutane nawa bane ‘yan sandan suka cafke yayin zanga-zangar ba.

Tun dai a safiyar Alhamis ne Sowore yayi kira ga ‘yan Najeriya da su fito zanga-zangar tare da daukar kyandira da fastoci inda za su nuna alhininsu a kan mulkin Buhari.

Frank Mba, kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya bai daga wayarsa ba yayin da ake ta kiransa domin jin tsokacinsa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here