Ambaliyar Ruwa ta yi Sanadin Mutuwar Mutane Sama da 200 a Malawi

Hukumomi a Malawi sun ce mutum fiye da dari biyu da ashirin aka tabbatar da mutuwarsu a ambaliyar ruwa da zaftarewar laka da guguwar da ke dauke da ruwan sama da iska da aka yi wa lakabi da Freddy ta haddasa.

Ana sa ran adadin zai karu ya yinda ma’aikatan ceto sun isa wuraren da guguwar ta yi kamari.

Wakiliyar BBC ta ce a karon farko bayan kwanaki da aka shafe ana tafka ruwan sama an wayi gari babu alamun haɗari a Blantrye wadda ita ce cibiyar kasuwancin ƙasar.

A yau ne ake sa ran shugaba Lazarus Chakwera zai zagaya wuraren da guguwar ta yi barna sosai.

Guguwar ta Freddy ta sa an yi ruwan saman da aka saba yi a watani shidda a cikin kwanaki shida a Malawi da Mozambique

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here