Amurka za ta Tallafa wa Falasɗinawan da Suka Rasa Muhallansu a Gaza

 

Babban sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken, ya ce Amurka za ta ba da tallafin fiye da dala miliyan 130 don taimaka wa Falasɗinawa da suka rasa matsugunansu a Gaza.

Mista Blinken na ganawa da shugabannin Qatar a birnin Doha, yayin ya ke ƙoƙarin ganin an tsagaita wuta.

Ƙasar Qatar – wadda shalkwatar siyasar Hamas ke cikinta – ita ce babbar mai shiga tsakani a rikicin.

Jami’in diplomasiyyar na Amurka na fuskantar ƙalubale da dama, kama daga tsaikon da aka samu a tattaunawar tsagaita wuta a Gaza zuwa ɓarkewar yaƙi tsakanin Isra’ila da Hezbollah.

Hamas ba ta sanar da sabon shugaba ba tun bayan kisan da Israila ta yi wa Yahya Sinwar a makon da ya gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here