ɓatagari Sun Tarwatsa Ma’aikatan Zaɓe da ‘Yan Jarida a kano

 

Rahotanni daga Kano a Najeriya sun bayyana cewa an samu wata hatsaniya a mazaɓar Ja’oji har wasu ma’aikatan zaɓe da ƴan jarida suka sha da ƙyar.

Wakilin BBC wanda ya kasance cikin ƴan jaridar da suka ɓuya a wani aji tare da malaman zaɓe, ya ruwaito cewa ɓatagarin sun kutsa cikin mazaɓar ne a dai-dai lokacin da jami’an INEC ke shirin fara ƙirgen ƙuri’u bayan da aka kammala zaɓe a mazaɓar.

Lamarin dai ya sa dole aka dakatar da aikin har zuwa lokacin da lamarin ya lafa.

Wakilin na BBC ya tabbatar da cewa mutanen da ke mazaɓar sun nemi mafaka a wata makaranta a lokacin da suka ga ɓatagarin.

Ya ce ya hango ƴan daban ɗauke da muggan makamai sun kai kawo a mazaɓar, inda ya ce sun tafi da na’urar VBAS guda ɗaya daga mazaɓar.

A cewarsa, jami’an tsaro ba su isa wajen ba a lokacin da ɓatagarin suka shiga mazaɓar.

Tuni dai aka samu lafawar al’amarin inda kuma aka soma ƙirgen ƙuri’un a wannan mazaɓa.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here