Gwamna Ganduja ya Mika Sandar Girma ga Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Bayero

 

Daga karshe Gwamna Ganduje ya gabatar da sandar girma ga Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado-Bayero.

Da yake jawabi yayin gabatar da sandar, Gwamna Ganduje ya yabawa cibiyoyin sarauta na jahar.

A halin da ake ciki, sarkin ya bukaci mutanen masarautar da su kara himma wajen shigar da yaransu cikin tsarin ilimin boko.

Bichi, Kano – Gwamna Abdullahi Ganduje na jahar Kano, a ranar Asabar, ya mika sandar girma ga Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado-Bayero, a matsayin Sarkin Bichi na biyu.

Masarautar ta Bichi tana daya daga cikin sabbin masarautun da gwamnatin Ganduje ta kirkiro.

Sauran sabbin masarautun da aka kirkiro sune Rano, Gaya da Karaye, baya ga majalisar masarautar Kano da ake da ita.

A ranar Juma’a ne Sarkin ya aurawa ‘yarsa dan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Yusuf.

Da yake jawabi bayan gabatar da sandar girma ga sarkin, Ganduje ya ce gwamnatin jihar ta yaba da gudummawar da masaratun ke bayarwa don inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a jahar.

Ganduje ya ce gudummawar da sarautar gargajiya suka bayar, ya sanya gwamnati ta kirkiro karin masarautun, da nufin fadada ci gaba zuwa yankunan da ke kasa.

Ya bukaci Sarkin da sauran sarakunan jahar, da su ci gaba da ba gwamnati gudunmawa wajen samar da tsaro ga dukiyoyi da rayukan jama’a.

Gwamnan ya bukaci Sarkin da ya ci gaba da zama uba ga duk talakawansa ba tare da nuna bambanci ba.

A jawabinsa na mika godiya, sabon Sarkin, yayi alkawarin yin adalci ga dukkan mutanen masarautar.

Ado-Bayero ya bukaci mutanen masarautar da su kara himma wajen shigar da yaransu cikin tsarin ilimi na asali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here