Hukumar NCC ta ƙayyade Mafi ƙarancin Shekarun Mallakar Layin Waya a Najeriya

 

Hukumar sadarwa ta NCC a Najeriya ta hana yi wa ‘yan ƙasar da shekarunsu bai kai 18 ba rajistan layukan waya.

A wani rahoto da ta wallafa hukumar NCC ta ce sai mutumin da ya kai 18 kawai za a rinka yiwa rajistan layuka.

NCC ta ce wannan mataki nata ya yi daidai da dokokin mallakar layin waya sashi na 70 na kudin bayanan sadarwar Najeriya na 2003.

A lokacin gabatar da wannan tsari gaban masu ruwa da tsaki da kamfanonin sadarwa ciki harda MTN, kamfanin ya bukaci a rage waɗannan shekaru.

MTN ya bukaci NCC ta tsayar da shekara 14 a matsayin mafi kakantar shekarun mallakar layin waya.

Sai dai NCC ta dage akan cewa dole sai mutum ya kai shekara 18 kafin ya mallaki layin waya harda rajista a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here