Babban Kwamitin Kungiyar Kasuwanci ta Duniya ta Sanar da Ranar Nadin Sabuwar Darakta Janar

 

Tsohuwar Ministar kudi a Najeriya, da yiyuwar ta kasance sabuwar Darakta-Janar na WTO.

Hukumar ta sanar da sabon nadin Darakta-Janar din zai gudana ranar 15 ga watan Fabrairu.

A baya, an bayyana tsohuwar ministar a matsayin ‘yar takara tilo da ta fito neman kujerar.

Babban Kwamitin Kungiyar Kasuwanci ta Duniya, WTO, ya ce zai duba yiwuwar nada Darakta-Janar na gaba mako mai zuwa ranar Litinin, Daily Nigerian ta ruwaito.

Ku tuna cewa tsohuwar Ministar Kudi ta Najeriya, Ngozi Okonjo-Iweala, ita ce ‘yar takara tilo da ta bayyana a wannan matsayi, biyo bayan sauka daga wani dan takarar wanda ya kasance Minista a Koriya a makon da ya gabata.

Kungiyar, a cikin wata sanarwa mai taken, ‘WTO General Council da za ta yi la’akari da nadin Darakta-Janar na gaba’ da ta wallafa a shafinta na intanet a ranar Talata, ta ce za a gudanar da taro na musamman na Babban Kwamishinanta a ranar 15 ga Fabrairu.

“Babban Kwamitin WTO zai yi taro na musamman a ranar 15 ga Fabrairu da misalin karfe 3:00 na yamma lokacin Geneva don yin la’akari da nadin Darakta-Janar na gaba. Taron zai gudana ne cikin tsari na kamala,” sanarwar ta kara da cewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here