Legas: Sojojin Najeriya Sunyi wa Gwamnan Tayin Dakaru

Gwamnan Jihar Legas ya ce rundunar sojojin Najeriya ta yi masa tayin ba shi taimakon dakaru domin daƙile zanga-zanga a jihar, a cewar rahoton Reuters.

An ruwaito Babjide Sanwo-Olu yana magana ne a hirarsa da wani gidan talabijin a yau Alhamis, yana mai cewa “shugaban sojoji ya kira ni ranar Laraba cewa idan ina buƙatar sojoji su zo za su fito kan tituna”.

Ya ce lamarin na kare lafiyar sana’o’i ne da kuma gine-ginen gwamnati, waɗanda wasu tsageru suka riƙa kai wa hari.

Ƙungiyoyin kare haƙƙi da kuma waɗanda suka shaida lamura da idanunsu sun ce sojoji sun buɗe wa masu zanga-zanga wuta ranar Talata. Amnesty International ta ce mutum 12 aka kashe a wuri biyu a Legas.

Sai dai rundunar sojojin ta musanta cewa dakarunta ne suka aikata harbe-harben.

Yanzu haka akwai dokar hana fita a birnin Legas ta awa 24 amma gwamnan ya ce akwai yiwuwar a sassauta ta ranar Juma’a idan abubuwa sun lafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here