Shugaban hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC, Ibrahim Magu ya mayar da hannun Kyauta baya, inda Yaki karbar kyautar Naira miliyan goma da Ganduje ya baiwa hukumar domin shirya gasar gudun yada kanin wani.

Magu ya bayyana cewar hukumar bata karbar tallafi na kudi daga hannun Gwamnoni. A ranar Litinin ne dai mai magana da yawun Gwamnan Kano Aminu Yassar ya bayyana cewar Gwamnan ya baiwa hukumar tallafin Naira miliyan goma dan ta shirya wata gasar tsere.

Sai dai a lokacin da yake mayar da martani kan batun, kakakin hukumar Tony Orilade ya bayyana cewar hukumar ya nesanta kanta daga karbar wadancan kudade da aka ce Ganduje ya bayar.

“Kokarin karya lagon hukumar ne na yaki da cin hanci da rashawa, wani Gwamna ya dauki kudi ya baiwa hukumar “ A cewar Orilade.

The post Magu yaki karbar kyautar Ganduje ta miliyan goma ga hukumar EFCC appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here