Adadin Mutanen da Suka Mutu Sakamakon Barkewar Baƙuwar Cuta a Zamfara

 

Adadin mutane da suka mutu sakamakon wata baƙuwar cuta da ta fi shafar yara da mata, a wasu yankuna na jihar Zamfara ya ƙaru zuwa 13.

Bincike daga majiyoyin asibitoci da na gwamnati ya nuna cewa an samu mutum 505 da suka kamu da cutar a sassan ƙananan hukumomin Maradun da Shinkafi da Gusau.

Sannan wani binciken, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, ya nuna cewa cutar ta bazu zuwa ƙananan hukumomin Isa da Zurmi a jihohin Sokoto da Zamfara.

An gano cewa an fara gano cutara ƙauyen Tsibiri a ƙamarar hukumar Maradun cikin watan Fabarairun wannan shekarar.

Wata majiya ta tabbatar cewa zuwa ranar Lahadi 12 ga watan Mayun 2024, mutum huɗu sun mutu, sai 228 da suka kamu da cutar da kuma marasa lafiya 10 da suke samun kulawa a cibiyar daƙile yaɗuwar cututtuka ta Shehu Shagari a Gusau.

Haka nan, a ƙaramar hukumar Shinkafi, an gano cutar a ƙauyen Galadi a Afrilu sakamakon matsanancin ciwon ciki da zazzaɓi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here