Rikicin Sudan: Najeriya za ta Kwashe ɗalibai 5000 Daga ƙasar

 

Ministan harkokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama ya shaida wa BBC cewa ofishin jakadancin ƙasar a Sudan yana ƙoƙarin shirya motocin bas-bas da za su kwashe ɗaliban ƙasar kimanin 5000.

Ana dai fatan kwashe ɗaliban ne zuwa kan iyakar Sudan da ƙasar Masar.

Daga ƙasar Masar ne kuma za a shirya yadda hukumomi za su fara kwaso ɗaliban a cikin jiragen sama zuwa gida Najeriya.

Sai dai zuwa yanzu, hukumomi a Najeriya ba su ce ga lokacin da za a fara wannan aiki na kwashe ɗaliban ba daga Sudan ɗin ba.

Sojojin Sudan da rundunar RSF ta masu kayan sarki na ci gaba fafata yaƙi a gwagwarmayar ɓangarorin biyu ta ƙwatar iko.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here