Oshiomhole ya Koka Kan Siyan Litar Man Fetur a N1,000

 

Tsohon gwamnan jihar Edo kuma tsohon shugaban APC na kasa, Adams Oshiomhole, ya koka kan siyan litar man fetur a N1,000.

Oshiomhole ya koka cewa duk da kashe fiye da naira tiriliyan kan tallafin mai, yan Najeriya na biyan fiye da farashin kasuwa.

A cewar Oshiomhole, N7trn kan tallafin mai bai kunshi kudaden ci gaban fetur ba, yana mai cewa dole a rike wani kan haka.

Adams Oshiomhole, tsohon shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, ya koka kan tsadar farashin man fetur a Najeriya.

Da yake jawabi a shirin Politics Today na Channels TV, tsohon gwamnan na jihar Edo, ya koka cewa ya siya litar mai kan N1,000.

Akwai mai hannu a karancin man fetur Oshiomhole

Oshiomhole ya ce lamarin ba abun dariya bane, yana mai cewa wani na da hannu a karancin man fetur a kasar nan.

Ya ce a yanzu haka, kasar na kashe kimanin naira tiriliyan 7 kan tallafin man fetur amma abun takaici shine cewa yawancin yan Najeriya na biyan fiye da farashin da ya kamata a siyar da mai a kasuwa.

Tsohon Shugaban kungiyar kwadago na kasar ya bayyana cewa duk da naira tiriliyan 7 na tallafin mai, akwai kuma wani kudin haraji na fetur, yana mai jaddada matsayinsa na farko cewa wasu ne ke da hannu a lamarin.

A cewarsa, idan yan Najeriya suna ganin ba sabon abu bane cewa mun saba samun karancin man fetur hatta a mulkin soja har zuwa Shugaba Olusegun Obasanjo, Yar’adua da Jonathan, ana iya cewa karancin mai ya zama dadaddiyar matsala amma wannan baya nufin abun yarda ne.

Tun a Janairu 2022 me kasar ke fama da matsalar karancin man fetur da tsadar farashi a yankuna daban-daban na kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here