‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 17 da Farar Hula 4 a Iyakar Mali, Burkina Faso da Nijar

 

Sojoji a ƙalla 17 ne da fararen hula huɗu aka kashe ranar Lahadi, sannan ba a ga wasu mutum tara ba, biyo bayan wani hari da ake zargin masu ikirarin jihadi ne suka kai.

Lamarin ya faru ne a garin Tessit da ke bakin iyakokin kasashe uku tsakanin Mali da Burkina Faso da Nijar, wajen da ake yawan samun hare-hare.

Wannan kiyasi na wadanda harin ya shafa na wucin gadi ne, kuma zai iya sauyawa, kamar yadda wata sanarwar rundunar sojin Mali a jiya Litinin ta ce..

Rundunar sojin ta kuma ce ta kashe mayaƙa bakwai da ake kyautata zaton ƴan ƙungiyar IS ne a yankin sahara, saboda taimakon da ta samu na amfani da jirgin mara matuƙi da kayan fashe-fashe da bama-bamai masu fasa motoci.

Sojin Malin ta kuma bayyana cewa sojoji 22 ne suka samu raunuka, sannan sun yi asarar motoci an kuma lalata shingayen tsaro.

Sannan a kalla wasu hare-hare biyu da mayakan sa kan suka kai sun yi sanadiyar rayukan fararen hula 12 ranar Asabar a tsakiyar Mali, da jami’an ƴan sanda biyar a ranar Lahadi a kudu maso yammacin kasar.

Kasar Mali na ci gaba da samun kalubalen ‘yan bindiga da ke ikirarin jihadi tun 2012, lamarin da a farko ya shafi arewacin kasar ne kadai.

Amma abun ya yaɗu zuwa tsakiya da kudancin Mali, da kuma makwabciya Burkina Faso da Nijar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here