Yadda Uwa ta Rasa Ranta a Kokarin Raba Faɗa Tsakanin ‘Ya’yanta Biyu

 

Wata mata mai suna Zainab Ibrahim ta rasa ranta a kokarin raba fada tsakanin ‘ya’yanta maza biyu, Inusa da Usman.

Duk da cewa babu cikakken bayani kan abin da ya hadasu, Inusa, bayanai na nuna cewa ya yi amfani da wuka wajen soka mahaifiyar a bisa kuskure a hannunta na dama.

Lamarin ya faru ne a unguwar Kpaduma da ke Asokoro a Abuja.

Wani mazauni unguwar Saliu Shehu ya ce an gagauta kai Zainab asibiti amma daga baya sai rai ya yi halinsa.

A lokacin da aka tuntube shi, kakakin ‘yansanda Abuja, Josephine Adeh, ya ce Inusa ya tsere amma ana bincike kan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here