ƙarancin Naira: An Baza ƴan Sanda a Legas Domin Daƙile Zanga-Zanga

 

An baza jami’an ƴan sanda a sassan birnin Lagos na Najeriya domin dakile tarzomar da ta ɓarke wadda ake kyautata zaton tana da nasaba da matsalar ƙarancin takardun kudin ƙasar na naira da ake fuskanta.

Rahotanin sun ce wasu manyan bankunan kasuwanci da ke birnin sun ci gaba da kasancewa a rufe.

An riƙa jin ƙarar harbe-harben bindiga kuma an toshe manyan hanyoyi da dama inda wasu suka yi amfani da tayoyin da ke ci da wuta.

Ƴan sanda sun ce an dawo da doka da oda a gundumar Mile 12, sannan sun ɗora alhakin tashin hankalin a kan ɓata-gari.

Jama’a na fushi a kan ƙarancin sababbin takardun kuɗin da aka sauya wa fasali, abin da ya haifar da zanga-zanga a farkon makon da ake ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here