Home DUNIYA Legas: Yadda Wasu jama’a su ka Fasa Rumbun Ajiyar Kayan Tallafin Korona

Legas: Yadda Wasu jama’a su ka Fasa Rumbun Ajiyar Kayan Tallafin Korona

0

Legas: Yadda Wasu jama’a su ka Fasa Rumbun Ajiyar Kayan Tallafin Korona

 

    Tirmitsitsi ya barke a Lagos, yayin da cincirindon mutane su ka fasa wani sito da aka ajiye kayan tallafin korona su ka rika jidar kayan abinci, a Monkey Village da ke Maza-maza, cikin unguwar Odofin.

Kayayyakin da aka rika jida din dai duk an buga masu tambarin ‘COCAVID’, NOT FOR SALE; wato kayan tallafin korona ne, ba na sayarwa ba ne.

Kayayyakin sun hada da shinkafa, macaroni, taliya, gishir, garri, sukari da kuma katan-katan na indomi.

Wani mazaunin unguwar ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa tun safe mazauna unguwar ke ta jidar kayan abincin.

“Da farko dai wasu mutane ne su ka isa sito din da safe su ka dauki wasu kayayyakin abincin. Dama sun saba zuwa kowane lokaci su na kwasa.” Haka wani mazaunin unguwar wanda ya roki kada a bayyana sunan sa, ya shaida wa PREMIUM TIMES.

“Lokacin da mutanen su ka lodi kayan abinci za su tafi, sai aka rika rokon su su bai wa wadanda ke wurin, amma su ka ki. Bayan sun tafi sai aka taru aka fasa sito din, kowa ya rika jida kawai. Gwamnati ta kimshe abinci, ba ta raba ba, ga kuma jama’a na cikin halin kunci.”

 

 

 

 

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest News
Ɓaraka tsakanin Buhari da Tinubu jita-jita ce kawai - Gwamna SuleRashin Tsaro: An Gudunar da Zanga-Zangar Lumana a Jihar FilatoKare Kai Daga 'Yan Bindiga: Martanin Gwamnan Jigawa ga TY DanjumaYadda Gobara ta yi ɓarna a KanoJihohin Najeriya da za su Fuskanci Ruwan Sama Hade da Tsawa a Kwanaki 3 - Nimet2027: Yadda Kawancen ‘Yan Adawa za ta kai ga ci - AtikuDalilin Ziyarar da Muka Kai wa Ganduje - Alhassan RurumStarlink: Tankiya ta Kaure Tsakanin Musk da Gwamnatin Afrika ta KuduHukuncin da Kotu ta Yanke wa Tsohon Shugaban Peru da MatarsaHukumar EFCC ta Fara Gudanar da Bincike Kan Dandalin CBEXGwamna Mutfwang ya Sanar da Haramta Kiwo da Daddare a Fadin Jihar FilatoAdadin Megawatt na Wutar Lantarki da Najeriya ta rage bai wa NijarMaganar Inganta Sinadarin Uranium Batu ne na Gaske - IranAn Sace Motar Ofishin Mai ba Shugaban ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu a AbujaJigon APC ya Mutu a Hannun yan Bindiga