Zanga-Zanga: Najeriya ta Gargaɗi ƴan ƙasarta Masu Shirin Zuwa Birtaniya 

 

Gwamnatin Birtaniya ta gudanar da taron gaggawa inda aka tattauna a kan yadda za a shawo kan hargitsi mai nasaba da kin jinin ƴan ci-rani a sassan ingila da kuma Arewacin Ireland.

Mako guda ke nan da mutane suka kai hari kan masallatai da otal-otal da kuma gidajen da masu neman mafaka ke zama.

Kazalika an balle shaguna da kuma jefa wa ƴansanda duwatsu.

Najeriya dai ta gargadi ƴan kasarta da ke shirin tafiya zuwa Ingila a kan su yi la’akari da abin da zai iya biyo baya.

Zanga -zangar da ake yi a kasar ta biyo bayan kisan da aka yi wa wasu yara mata uku a makon da ya wuce.

Jita-jitar da aka riƙa yaɗawa a shafukan sada zumunta ta ɗora alhakin kisan yaran kan wani ɗan ci-rani.

An kama mutane fiye da 250.

Mnistan cikin gidan Birtaniya, Yvetter Cooper, ya ce duk mutanen da suka yi tarzoma za su fuskanci fushin hukuma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here