Atiku ya Nada Shekarau, Saraki, da Wasu a Matsayin Masu ba Shi Shawara

Ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya nada sabbin masu ba shi shawara na musamman don karfafa yakin neman zaɓensa a shekarar 2023.

Wadanda aka nada sun hada da tsohon gwamnan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, tsohon shugaban majalisan dattawa, Dr.Bukola Saraki da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Sanata Pius Anyim a matsayin masu ba shi shawara na musamman.

Sauran su ne tsohon gwamnan jihar Osun, Prince Olagunsoye Oyinlola da kuma sanata Ehigie Uzamere.

Sai kuma tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Prince Uche Secondus.

Nadin nasu zai fara aiki ne nan take.

Atiku Abubakar ya umarci sabbin wadanda aka nada da su yi amfani da gogewar su ta siyasa domin su tabbatar cewa an samu gagarumar nasara a yakin neman zaɓen 2023.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here