Za mu Bawa Mutanen Shekarau da Suka Koma Jam’iyyar PDP Mukamai – Ayu

 

Shugaban babbar jam’iyyar adawa a Najeriya PDP, Iyorchia Ayu ya ce za su baiwa mutanen malam Ibrahim Shekarau da suka koma jam’iyyar mukamai lokacin nadin sabbin shugabannin jam’iyyar a jihar bayan rushe na da.

Shugaban na jam’iyyar PDP ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da BBC, inda ya ce za su baiwa mutanen Shekarau din mukamai ne sabo da a yanzu su ‘ya’yan jam’iyyar ne.

Ya kuma ce za a saka mutanen Ibrahim Shekarau ne a dukkan matakan shugabancin jam’iyyar a Kano kama daga jiha zuwa kananan hukumomi.

A ranar Litinin din nan ne, tsohon gwamnan na Kano ya sanar da ficewarsa a hukumance daga jam’iyyar NNPP zuwa PDP saboda abin da ya kira “rashin adalci” da Rabiu Kwankwaso ya yi musu, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa kuma jagoran jam’iyyar NNPP.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here