Bayan Kashe Mutane 50: Gwamnatin Burkina Faso za tai Zaman Makoki na Kwana 3

Gwamnatin Burkina Faso ta sanar da zaman makoki na kwana uku daga yau Talata bayan kashe aƙalla mutum 50 a ƙarshen mako a arewacin ƙasar.

Shugaban mulkin sojan ƙasar Laftanar Kanal Paul-Henri Damiba ne ya bayar da umarnin yin zaman makokin.

A ranar Litinin ne gwamnatin ƙasar ta ce an kashe farar hula 50 a wani hari da wasu yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka kai a yankin Seytenga inda gwamnatin ta ce akwai yiwuwar adadin mutanen zai iya ƙaruwa.

Wasu rahotanni sun ce adadin mutanen da suka rasu ya kai zarta 10.

A lokacin zaman makokin, za a rage tsawon tutocin ƙasar a kusan duka gine-ginen gwamnati da kuma ofisoshin jakadancin ƙasar a wasu ƙasashe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here