CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi Don Magance Karancin Takardun Naira

 

Babban bankin Najeriya CBN ya umarci bankunan ƙasar da su yi aiki a yau Asabar da kuma gobe Lahadi domin tabbatar da cewa takardun kuɗaɗen naira sun wadata a hannun jama’a.

A wata sanarwa da CBN ya wallafa a shafin na Tuwita, ya ce ya fito da maƙudan takardun naira ne a bankunan ƙasar da kuma na’urorin cirar kudi ta ATM domin magance matsalar ƙarancin kuɗin a ake fama da shi a fadin ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa CBN ya bayar da umarnin ɗaukar takardun kuɗaden daga rassansa zuwa bankunan kasuwanci da ke fadin ƙasar

Ta ƙara da cewa bankunan kasuwancin ƙasar sun samu maƙudan takardun kuɗaɗe domin rarraba wa abokan huldarsu, da nufin wadatar kuɗade a hannun jama’a.

Sanarwar ta ci gaba da cewa babban bankin ƙasar ya umarci bankunan kaswunci da su sanya takardun kuɗaden cikin na’urorin cirar kudinsu na ATM, domin sauƙaƙa wa kwastomominsu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here