Dalilin Taron Gwamnoni 36

Gwamnonin Jahohi za su yi wani zama a dalilin matsalar rashin tsaro.

Kungiyar NGF za ta zauna ne a Ranar Laraba bayan harin Zabarmari.

Gwamnan Kaduna da babban bankin CBN zasu yi jawabi wajen taron.

Vanguard ta ce gwamnonin jihohi 36 na kasar nan a karkashin kungiyar NGF za su zauna a gobe, 2 ga watan Disamba, 2020, a dalilin sha’anin tsaro.

Babban makasudin wannan taro shi ne gwamnonin su fito da sabon tsari a game da harkar tsaro.

A halin yanzu ana fama da yawan hare-haren ‘yan bindiga, ta’addancin Boko Haram da garkuwa da mutane da ake yi a jihohi da-dama a Najeriya.

Ana cikin wannan yanayi sai ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai hari a kauyen Zabarmari, jihar Borno, inda su kayi wa mutane har 43 yankan-rago.

Lamarin rashin tsaro yana damun jihohin kasar. Wannan zama da za ayi a ranar Laraba shi ne karo na 22 da kungiyar gwamnonin za ta zauna.

Daga cikin batutuwan da za a tattauna a zaman gobe, akwai kudirin ruwa da ya kawo ce-ce-ku-ce da Ministan harkokin ruwa zai yi karin-haske a kai.

Bayan jawabi daga Suleiman Hussein Adamu, takwaransa a ma’aikatar shari’a, Abubakar Malami zai bayyana inda aka kwana kan kudin harajin hatimi.

Haka zalika babban gwamnan CBN, Godwin Emefiele da gwamna Nasir El-Rufai za suyi magana kan yadda ake yin ayyuka da kudin asusun fansho.

Darektar NGF, Asishana Bayo Okauru, ta ce za a fara taron ne da karfe 2:00 na rana, amma gwamnoni za su samu damar hallara ta kafar gizo kafin nan.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here