ɗan Majalisar Dokokin Jihar Katsina ya Rasu a Saudiyya

 

Wani ɗan majalisar dokokin jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya, Dr Ibrahim Aminu Kurami, ya rasu a Saudiyya.

Ɗan majalisar mai wakilar mazaɓar ƙaramar hukumar Bakori ya je Saudiyyan ne don gabatar da aikin Umara, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Wata majiya daga iyalansa ta shaida wa jaridar cewa ya rasu ne bayan fama da gajeriyar rashin lafiya a Madina.

Marigayin ya rasu ya bara mata biyu da ƴaƴa 11 da kuma jikoki uku.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here