Tsohon Gwamnan Jahar Cross Rivers, Donald Duke ya Sauya Jam’iyya

 

Jam’iyyar PDP tayi babban kamu yayin da tsohon gwamnan jahar Cross Rivers, Donald Duke, ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar.

An tabbatar da komwar Mr. Duke zuwa jam’iyyar PDP ne yau Laraba, bayan ɗaukar kwanaki ana yaɗa jita-jita.

Wannan na zuwa ne biyo bayan sauya sheƙar gwamnan jahar Cross Rivers, Ben Ayade, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Donald Duke, tsohon gwamnan jahar Cross Rivers ya sauya sheƙa zuwa babbar jam’iyyar Adawa PDP, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Jaridar ta ruwaito cewa shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar PDP a yankin kudu maso kudancin ƙasar nan, Effiok Cobham, shine ya bayyana haka ranar Laraba 26 ga watan Mayu.

Da aka tambayeshi akan raɗe-radin da ake cewa tsohon gwamnan ya dawo PDP, Mr. Cobham yace: “Eh, harma yayi rijista da jam’iyya.”

Legit.ng ta gano cewa, Duke ɗan asalin jam’iyyar PDP ne kafin ya fice a shekarar 2018 yakoma SDP, inda aka tsayar dashi takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2019.

Mr. Duke ya riƙe muƙamin gwamnan jahar Cross Rivers na tsawon zango biyu daga Shekarar 1999 zuwa 2007. Wannan na zuwa ne bayan gwamnan jahar Cross Rivers, Ben Ayade, ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

Gwamnan ya bada wannan sanarwar ne ranar Alhamis 20 ga watan Mayu, lokacin taron sa da wasu gwamnonin APC waɗanda suka kai masa ziyara a gidan Gwamnatin jahar.

Yayin da yake bada sanarwar ficewa daga PDP zuwa APC, gwamna Ayade yace wannan matakin da ya ɗauka zaisa jahar Cross Rivers ta samu ayyuka da dama daga gwamnatin tarayya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here