Hukumar EFCC ta Kama Mutane a Kaduna,Kano da Abuja Bisa Zargin Sayen Kuri’a

 

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya (EFCC), ta kama wata mata da katunan zaɓe 18 a jihar Kaduna da kuma wasu a Kano da Abuja.

Jami’an hukumar ne suka kama matar da safiyar yau a unguwar Badarwa da ke Kaduna bayan kai wani samame.

An kuma samu wata takarda ɗauke da jerin sunayen masu zaɓe guda 17 da asusun ajiyarsu na banki da lambobinsu na waya a matsayin waɗanda ke da damar yin zaɓe a mazaɓar Badarwa/Malali 01 da 08 da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa.

An kama ta ne lokacin da jami’an na EFCC suka bad-da-kama, inda suka nuna cewa za su sayar da katunansu na zaɓe.

A halin yanzu dai tana hannun jami’an na EFCC a shiyyar Kaduna, inda suke ƙoƙarin gano wasu mutane da ke tare da ita waɗanda ta ce su ma suna karɓar katunan zaɓen mutane da kuma ba su kuɗi ta amfani da POS da kuma tura kuɗin ta intanet.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here