Gidauniyar Malam Inuwa ta Rabawa Marayu 100 Tallafin Turmin Atamfa 

 

A ƙoƙarin da ta ke kan cigaba da yi wajen ganin ta kyautatawa marayu a Jihar Jigawa a wannan wata na Ramadan mai albarka, Gidauniyar Malam Inuwa wacce mai girma shugaban hukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE) ya assasa, ta rabawa marayu mata (100) tallafin turmin Atamfa domin hidimar sallah a ƙaramar hukumar Haɗejia da ke Jihar Jigawa.

Rabon wanda aka gudanar a yammacin wannan rana, a ofishin gidauniyar da ke kan titin Garun-Gabas, Haɗejia, ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin shugabannin gidauniyar, da kwamitin marayu na ƙaramar hukumar waɗanda su ka zaƙulo marayun da su ka fi buƙatar temako a mazaɓun yankin gabaɗaya.

Marayun da su ka halarci wurin rabon su ka karɓa, da kuma wakilan marayun waɗanda su ka karɓa musu, gabaɗaya sun bayyana godiya da farin cikinsu tare da addu’ar fatan alkhairi ga mai girma shugaban hukumar ta (NITDA), Malam Kashif gami da fatan Allah Ya ji ƙan mahaifin nasa, Malam Inuwa Ya ƙara arziƙi.

Talata, 19 ga watan Afrelu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here