Manyan ‘Yan Najeriya Masu Fada a Aji 20 da Suka Halarci Daurin Auran ‘Dan Shugaba Buhari

 

Manyan jiga-jigan siyasan Najeriya sun dira kasar Bichi, a jahar Kano domin halartan daurin auren ‘dan Buhari daya tilo, Yusuf, da diyar sarkin Bichi, Zahra Bayero.

Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ibrahim Pantami, ne ya daura aure a Masallacin kasar Bichi.

Yayinda babban attajiri, Alhaji Aminu Dantata, ya bada auren a madadin iyalan Sarkin Bichi; dan uwa kuma babban aminin Buhari, Malam Mamman Daura, ya karba aure matsayin wakilin ango kuma madadin shugaba Buhari.

An dade ba’a daurin auren da ya tattara manyan masu fada a aji irin wannan ba.

Ga jerin wasu sannannu da suka halarci daurin aure:

1. Shugaba Muhammadu Buhari

2. Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo

3. Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan.

4. Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar

5. Tsohon shugaban kasan jamhurriyar Nijar, Mohammadou Issoufou

6. Alhaji Aminu Dantata

7. Malam Mamman Daura

8. Gwamnan jahar Kano, Abdullahi Ganduje

9. Shugaban kungiyar gwamnoni kuma gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi

10. Gwamnan jahar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu.

11. Gwamnan jahar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal

12. Gwamnan jahar Jigawa, Muhammad Badaru Talamiz

13. Gwamnan jahar Yobe, Mai Mala Buni

14. Mataimakin gwamnan Kano, Yusuf Gawuna

15. Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle

16. Gwamnan Borno, BabaganMai a Umara Zulum

17. Sanata Ahmad Sani Yarima

18. Sanata Ali Ndume

19. Malam Nuhu Ribadu

20. Shugaban masu rinjaye a majalisa, Ado Doguwa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here