An Kaiwa Gidan Shugaban Kwamitin Yaƙin Neman Zaben Atiku Hari a Jihar Ribas

 

‘Yan bindiga sun kai hari gidan shugaban kwamitin yaƙin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Lee Maeba a jihar Ribas.

Sun lalata motoci sama da biyar a gidan, a harin da suka kai jiya Alhamis da safe.

Shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar ta PDP a Ribas, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels faruwar lamarin, inda ya ce wani mutumi ne ya kira sa tare da fada masa cewa ya yi taka tsan-tsan kan yunkurin kawo harin.

Ya ce an kawo harin ne jim kadan bayan fitar sa zuwa gidan surukansa, inda suka yi ta harbe-harbe a kofar gidan tare da daure maigadin gidan.

An ruwaito raunata mutum akalla uku yayin harin.

Babu wata sanarwa daga wajen ‘yan sanda kan harin lokacin hada rahoton, sai dai, gwamnatin Ribas ta umurci jami’an tsaro da su gudanar da bincike kan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here