An Kama ‘Yan Damfarar Intanet 2 da Ake Zargi da Wawushe Sama da N500m

 

Wasu da ake zargin cewa masu damfara ne ta intanet sun wawushe naira miliyan 523,337,100, daga asusun wani kwastoma, zuwa asusuna daban-daban har goma 18.

Mai magana da yawun sashe na musamman kan ayyukan damfara na rundunar ‘yan sanda a jihar Legas, SP Eyitayo Johnson, ya ce daga baya ‘yan damfarar na intanet sun aike da kudin zuwa sama da asussa 200 a bankuna daban daban.

Ya kuma kara da cewa sun yi hakan ne tsakanin ranakun 23 ga watan Afrilu zuwa 25 ga watan na Afrilu, kuma tuni sun kama mutum biyu da suke tuhuma da hannu a mummunan aikin.

Kawo yanzu an iya kwato sama da naira miliyan 160, yayin da ake ci gaba da neman mambobin wannan kungiya.

SP Eyitayo ya ce za su gurfanar da wadanda suka fara shiga hannu gaban kotu da zarar sun kammala nasu binciken.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here