ƙarancin Naira: Ana Zanga-Zanga a Sassan Jihohin Najeriya

 

Tarzoma ta ɓarke a wasu sassan jihar Lagos da safiyar yau Juma’a inda wasu da ake zargin ɓata-gari ne suka bazama manyan ttituna suna zanga-zanga a kan ƙarancin takardun kuɗin ƙasar na naira.

Jaridar Vanguard wadda tana daga cikin jaridun ƙasar da suka ruwaito, labarin masu zanga-zangar sun yi cincirundo a unguwannin Mile-12 da Ketu da Ojota, a kan titin Ikorodu, Iyana-Ipaja da misalin ƙarfe shida na safe, kafin ta fantsama zuwa wasu yankunan kamar Agege da Iyana-Iba.

Masu motoci da ke kan hanyarsu ta zuwa aiki sun riƙa juyawa a firgice saboda masu zanga-zangar sun rika kunna wa tayoyin da sauran abubuwa wuta suka kashe hanya.

Masu motoci sun tsaya curko-curko a babbar hanyar Lagos/Ibadan sakamakon zanga-zangar.

Tun da farko jaridar ta ruwaito cewa an samu irin wannan tarzoma a jihohin Edo da Oyo da Ogun duka saboda ƙarancin naira da kuma na man fetur.

Ita ma jaridar Punch ta ruwaito cewa ana samun rahotannin irin wannan zanga-zanga a wasu sassan Port Harcourt, babban birnin jihar Ribas.

Rahoton ya ce masu zanga-zngar na cinna wa bankuna wuta

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here