Zaben Gwamnoni: Jam’iyyar LP ta Marawa PDP Baya a Jihar Rivers

 

Jam’iyyar Labour reshen jihar Rivers da kungiyar gangami ta Obi-dient Movement sun bayyana goyon bayansu ga dan takarar gwamnan PDP a jihar, Sim Fubara a zaben 11 ga watan Maris.

Shugaban jam’iyyar Labour na jihar, Dienye Pepple ne ya bayyana hakan, inda ya ce shawarin ya zo ne duba da samar da daidaito da adalci a jihar, The Nation ta ruwaito.

Pepple, wanda ya jagoranci sauran shugabannin jam’iyyar don marawa Fubara a Fatakwal ya bayyana cewa, mazabarar Fubara ta Kudu maso Gabas har yanzu bata samar da gwamna ba a Rivers.

Ya ce, dukkan ‘yan jam’iyyar Labour sun yanke shawarin kada kuri’unsu ga dan takarar gwamnan a zaben mai zuwa don ci gaban jihar.

Karin bayani na nan tafe…

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here