Mutane 4 Sun Rasa Rayukansu a Jihar Kogi Bayan Cin Amala

 

Rahotanni daga garin Mopa da ke jihar Kogi a Najeriya, na cewa wasu mutum hudu yan gida daya sun mutu, bayan kammala cin Amala.

Mutanen sun hada da mahaifi da ‘ya’yansa biyu mata, da kuma wani dan uwansu.

Kamar yadda rahotannin suka nuna mutanen sun kamu da rashin lafiya ne cikin dare, bayan kammala cin abincin.

Sai dai matar mutumin har yanzu tana jinya a asibiti.

Mai magana da yawun gwamnatin jihar Kogi, Kingsley Fanwo, ya fada wa BBC cewa an umurci jami’an tsaro da na lafiya da su fara bincike kan lamarin ba tare da bata lokaci ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here